Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin da ƙasarsa ta kai kan wuraren nukiliyar Iran “hari ne mai ƙarfi sosai kuma ya lalata cibiyoyin nukiliyar Iran.
Trump ya ce In da ba a lalata cibiyoyin nukiliyar Iran ba, da ba ta amince da tsagaita wuta ba” ko ta amince da sasanci.
Sakataren harkokin waje Amurka, Marco Rubio, ya tsoma baki dangane da rahoton da hukumar leƙen asiri ta ƙasar Pentagon ta fitar, yana mai cewa rahoton na dogara ne da bayanan da wani ɗan buƙulu ya bayar, inda ya ce “wannan wasa ne kawai da wasu ke yi da bayanan sirri.”
Rubio ya ƙara da cewa an lalata “wurin da ake canza sinadaran nukiliya zuwa makamai,” kuma yanzu ba a iya ganin wurin gaba ɗaya. Sai dai bai bayyana inda wurin yake ba.