fidelitybank

Ba da yawun mu ‘yan tsohuwar CPC suka goyi bayan Tinubu ba – Malami

Date:

Tsohon Ministan Shari’a na Najeriya, Dakta Abubakar Malami, SAN, ya yi watsi da iƙirarin da wasu ƴan tsohuwar jam’iyyar CPC – da ta narke cikin haɗakar APC – suka yi na nesanta tsohuwar jam’iyyar daga ficewa daga haɗakar.

A farkon makon nan ne wani tsagin tsohuwar jam’iyyar CPC ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamnan Nasarawa, Umaru Tanko Almakura suka yi taro a Abuja, inda suka jaddada goyon bayansu ga gwamnatin shugaba Tinubu tare da nesanta kansu daga ficewa daga APC.

Daga cikin waɗanda suka harci taron har da tsohon gwamnan Katsina, Aminu Bello Masari da tsohon ministan Ilimi, Mallam Adamu Adamu da Hon Farouk Adamu Aliyu, tsohon ɗan majalisar daga jihar Jigawa da wasu ƙusushin tsohuwar CPCn.

To sai toshon Ministan ya yi watsi da wannan iƙirari da tsagin Almakuran suka yi, yana mai bayyana matsayar tasu da ta raɗin kai ba da yawun tsohuwar tafiyar CPCn ba.

Cikin wata sanarwa da kakakin tsohon ministan, Muhammad Bello Doka ya fitar, ya ce jagorancin tsohuwar jam’iyyar CPCn ne kawai ke da alhakin fitar da matsayar tsohuwar jam’iyyar kan kan batun fita daga APC, ba tsagin su Almakura ba.

Malami ya zargi Tanko Al-Makura da Adamu Adamu da Aminu Bello Masari da kuma Farouk Adamu Aliyu ya janye jikinsu daga jikin tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari.

Dangane da batun komawarsa jam’iyyar SDP kuwa, Malami ya ce aikin masu yaɗa jita-jita ne, amma ya ce yana kan tattaunawa da magoya bayansa kan batun.

“Malami fitaccen mutum ne a Najeriya, don haka ba zai fice daga jam’iyya a asirce ba, har yanzu yana APC, amma yana ci gaba da tattaunawa da magoya bayansa, idan ya kammala kuma zai bayyana matsayinsa”, in ji kakakin tsohon ministan.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp