fidelitybank

Ba bu wani zargin shirya garkuwa da mutane a Abuja – ‘Yan Sanda

Date:

‘Yansanda sun musanta raɗe-raɗin zargin shirya garkuwa da mutane a jami’ar Abuja.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke shirin gudanar da bukukuwan cikar ƙasar shekara 64 da samun ‘yancin kai cikin mako mai zuwa.

A ‘yan ƙwanakin nan ne dai zargin shirya garkuwa da mutane a jami’ar ya karaɗe shafukan sada zumunta.

To sai dai cikin wata sanarwa da kakakin ‘yansandan birnin Abuja, Josephine Adeh ta fitar ta ce rahotonnin shirya harin ba gaskiya ba ne.

“Rundunar ‘yansandan Abuja, na son fayyace wa al’umma cewa waɗannan rahotonni ba gaskiya ba ne, labarai ne irin na ƙanzon kurege, kuma marasa tushe, da aka ƙirƙira da nufin haifar da fargaba da tsoro a tsakanin mazauna Abuja da na jami’ar”, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Josephine Adeh ta ƙasa da cewa tuni rundunar ta ƙara girke jami’an ‘yansandan da kayan aiki a faɗin birnin da kewaye.

A baya-bayan nan birnin na Abuja ya fuskanci karuwar matsalar garkuwa da mutane. Inda mazaune unguwannin da ke wajen birnin ke cewa masu garkuwar na addabarsu a wasu lokuta ba tare da ɗaukin jami’an tsaro ba.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp