fidelitybank

Ba batun harajin Tinubu ba ne ya janyo ɗauke auren dan Barau daga Kano – Iyalan Amarya

Date:

Iyalan gidan marigayi Ado Bayero sun musanta raɗe-raɗin da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta cewa sun ɗauke bikin ɗauren auren ‘yarsu, Maryam Nasir Ado Bayero da ɗan mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Jibrin (Abba) Barau I Jibrin, saboda dambarwar da ta biyo bayan gabatar da ƙudurin harajin Shugaba Tinubu da aka yi a majalisar.

A wata sanarwa da shugaban kwamitin tsare-tsaren bikin, na ɓangaren iyalan amarya, Alhaji Aminu Babba Dan Agundi, Sarkin Dawaki Babba na Kano, ya fitar a jiya Litinin, ya ce an sauya wajen ɗaurin auren ne, daga Kano zuwa Abuja, ba don tankiyar da ƙudurin harajin ya janyo ba.

Alhaji Aminu ya kuma ce wannan shawara ce ta iyayen amarya ba wai ta iyayen ango ba, kamar yadda ake yaɗawa.

Ya ce kamar yadda al’adarsu ta tanada, aihakin iyayen amarya ne zaɓar rana da wajen da za a ɗaura aure ba iyayen ango ba.

Ya ƙara da cewa tun makonin da suka gabata aka sauya wajen ɗaurin auren da za a yi ranar Juma’a 13 ga watan nan na Disamba, domin sauƙaƙa wa manyan baƙin da suka nuna sha’awarsu ta halarta daga sassan ƙasar da kuma waje.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp