fidelitybank

Ba a tsayar da ranar ƙaddamar da rahoton Orosanyae ba – Gwamnati

Date:

Femi Gbajabiamila, shugaban ma’aikatan shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya bayyana cewa babu wani lokaci da aka tsayar don ƙaddamar da rahoton Steve Oronsaye.

Da yake magana bayan wata ziyarar aiki da ya kai hedkwatar hukumar da ke sa ido kan kudaɗen shiga da ake samu wajen haƙƙo ma’adinai (NEITI) a Abuja, Gbajabiamila ya tabbatar da cewa gwamnatin tarayya na aiki tuƙuru kan rahoton tare da musanta cewar an ajiye rahoton kuma ba za ayi amfani da shi ba

Ya kuma jaddada buƙatar yin taka-tsantsan, inda ya bayyana cewa yayin da aka kafa kwamitin da zai duba rahoton, za a fara aiwatar da shi nan ba da daɗewa ba.

Rahoton Oronsaye, wanda aka gabatar a shekarar 2012, ya ba da shawarar ragewa tare da haɗa ma’aikatu, kwamitoci, da hukumomi 541 na Najeriya ta hanyar rage su zuwa 161, da haɗe 52, da kuma soke 38 don rage kashe kuɗin gwamnati da kuma tabbatar da inganta ayyuka.

Don haka ne Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ta amince da aiwatar da rahoton gadan-gadan a cikin watan Fabrairu a wani ɓangare na matakan rage tsadar kayayyaki, aiwatarwar na samun tafiyar hawainiya.

Amma duk da cewa an kafa kwamitin mutum takwas domin aiwatar da shirin cikin mako 12, sai dai an yi wata shida ke nan kuma babu wani muhimmin mataki da aka ɗauka.

Maimakon haka, gwamnati ta kafa ma’aikatar kula da kiwon dabbobi daga ma’aikatar noma, wanda hakan ya jawo ra’ayoyi mabambanta.

Rahoton ya samo asali ne daga kwamitin da shugaban ƙasa na wancan lokacin Goodluck Jonathan ya kafa a shekarar 2011 domin magance matsalolin da hukumomin gwamnati ke fuskanta inda Oronsaye ne shugaba kwamiti ɗin.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp