Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta ce har yanzu ba a mika mata takardar shedar kofi na ainihin da babban kotun tarayya da ta kori Gwamna Dave Umahi na jihar Ebonyi da mataimakinsa, Cif Kelechi Igwe.
Mista Festus Okoye, kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) a Abuja ranar Talata.
Okoye ya ce, hukumar za ta gana kuma za ta yanke hukunci idan ta samu kwafin gaskiya na hukuncin kotun.
“Ba a ba hukumar kwafin hukuncin da aka ce ba. Hukumar za ta gana kuma za ta yanke hukunci idan aka ba ta kofin hukuncin na ainihi,” in ji Okoye.
Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, karkashin jagorancin mai shari’a Inyang Ekwo, a ranar Talata, ta umurci Gwamna Umahi da ya bar ofishin, bayan ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.
Mai shari’a Ekwo, a hukuncin, ya kuma umarci Dr Eric Igwe da ya daina bayyana kansa a matsayin mataimakin gwamnan jihar.