Mataimakin kwamandan hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, Musa Sani Bakura, ya bayyana cewa, Najeriya ba ta samu matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi ba a lokacin aikin hajjin bara.
Ya ce hukumar ba ta samu korafe korafe daga hukumomin Saudiyya na ‘yan Najeriya da ke fitar da kwayoyi ko kuma an kama su da kwayoyi ba.
Shugaban hukumar ta NDLEA ya bayyana cewa a aikin Hajjin bana, sun dauki kwakkwaran matakai na tabbatar da cewa babu wanda ke safarar kwayoyi zuwa kasa mai tsarki, ciki har da masu fitar da goro a cikin manya-manyan, wanda kuma aka haramta.
Karanta Wannan: Mahajjata miliyan 2 za su yi aikin bana a Saudiyya
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kano ta fara gangamin wayar da kan Alhazai na shekarar 2023 kamar yadda aka ce hukumar ta samu sama da kashi 70 cikin 100 na ajiya na aikin Hajji.
Da yake jawabi yayin wani taron wayar da kan jama’a da hukumar ta shirya, Sakataren zartarwa, Muhammad Abba Dambatta, ya ce gwamnatin jihar Kano ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da ayyukan Hajji da ke tafe ba tare da tangarda ba.
Dambatta ya yi nuni da cewa Kano ta samu guraben aikin Hajji 5,902 daga Hukumar Alhazai ta kasa, NAHCON, a shekarar 2023, kuma daga cikin su kusan 4000 sun ajiye kudadensu, wanda hakan ya nuna cewa sun jajirce wajen gudanar da shirye-shiryen.
Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Amin Ado Bayero, ya ce kwakkwaran matsayar da hukumar jin dadin alhazai ta Kano da gwamnati suka dauka ya taimaka matuka gaya wajen ganin an samu matsala a bara.
Ya bukaci maniyyatan 2023 da su kara zage damtse wajen addu’o’i domin Najeriya ta fita lafiya daga matsalolin da take fuskanta.