fidelitybank

Ba a kama dan Najeriya da kwaya ba a aikin Hajjin bara – NDLEA

Date:

Mataimakin kwamandan hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, Musa Sani Bakura, ya bayyana cewa, Najeriya ba ta samu matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi ba a lokacin aikin hajjin bara.

Ya ce hukumar ba ta samu korafe korafe daga hukumomin Saudiyya na ‘yan Najeriya da ke fitar da kwayoyi ko kuma an kama su da kwayoyi ba.

Shugaban hukumar ta NDLEA ya bayyana cewa a aikin Hajjin bana, sun dauki kwakkwaran matakai na tabbatar da cewa babu wanda ke safarar kwayoyi zuwa kasa mai tsarki, ciki har da masu fitar da goro a cikin manya-manyan, wanda kuma aka haramta.

Karanta Wannan: Mahajjata miliyan 2 za su yi aikin bana a Saudiyya

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kano ta fara gangamin wayar da kan Alhazai na shekarar 2023 kamar yadda aka ce hukumar ta samu sama da kashi 70 cikin 100 na ajiya na aikin Hajji.

Da yake jawabi yayin wani taron wayar da kan jama’a da hukumar ta shirya, Sakataren zartarwa, Muhammad Abba Dambatta, ya ce gwamnatin jihar Kano ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da ayyukan Hajji da ke tafe ba tare da tangarda ba.

Dambatta ya yi nuni da cewa Kano ta samu guraben aikin Hajji 5,902 daga Hukumar Alhazai ta kasa, NAHCON, a shekarar 2023, kuma daga cikin su kusan 4000 sun ajiye kudadensu, wanda hakan ya nuna cewa sun jajirce wajen gudanar da shirye-shiryen.

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Amin Ado Bayero, ya ce kwakkwaran matsayar da hukumar jin dadin alhazai ta Kano da gwamnati suka dauka ya taimaka matuka gaya wajen ganin an samu matsala a bara.

Ya bukaci maniyyatan 2023 da su kara zage damtse wajen addu’o’i domin Najeriya ta fita lafiya daga matsalolin da take fuskanta.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp