fidelitybank

Ba a kama dan Najeriya da kwaya ba a aikin Hajjin bara – NDLEA

Date:

Mataimakin kwamandan hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, Musa Sani Bakura, ya bayyana cewa, Najeriya ba ta samu matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi ba a lokacin aikin hajjin bara.

Ya ce hukumar ba ta samu korafe korafe daga hukumomin Saudiyya na ‘yan Najeriya da ke fitar da kwayoyi ko kuma an kama su da kwayoyi ba.

Shugaban hukumar ta NDLEA ya bayyana cewa a aikin Hajjin bana, sun dauki kwakkwaran matakai na tabbatar da cewa babu wanda ke safarar kwayoyi zuwa kasa mai tsarki, ciki har da masu fitar da goro a cikin manya-manyan, wanda kuma aka haramta.

Karanta Wannan: Mahajjata miliyan 2 za su yi aikin bana a Saudiyya

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kano ta fara gangamin wayar da kan Alhazai na shekarar 2023 kamar yadda aka ce hukumar ta samu sama da kashi 70 cikin 100 na ajiya na aikin Hajji.

Da yake jawabi yayin wani taron wayar da kan jama’a da hukumar ta shirya, Sakataren zartarwa, Muhammad Abba Dambatta, ya ce gwamnatin jihar Kano ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da ayyukan Hajji da ke tafe ba tare da tangarda ba.

Dambatta ya yi nuni da cewa Kano ta samu guraben aikin Hajji 5,902 daga Hukumar Alhazai ta kasa, NAHCON, a shekarar 2023, kuma daga cikin su kusan 4000 sun ajiye kudadensu, wanda hakan ya nuna cewa sun jajirce wajen gudanar da shirye-shiryen.

Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Amin Ado Bayero, ya ce kwakkwaran matsayar da hukumar jin dadin alhazai ta Kano da gwamnati suka dauka ya taimaka matuka gaya wajen ganin an samu matsala a bara.

Ya bukaci maniyyatan 2023 da su kara zage damtse wajen addu’o’i domin Najeriya ta fita lafiya daga matsalolin da take fuskanta.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp