fidelitybank

Ba a cimma matsaya ba tsakanin Gwamnati da Kungiyoyin Kwadago

Date:

Ba a cim ma matsaya ba a taron tattaunawa tsakanin haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙwadago da gwamnatin Najeriya game da tsadar rayuwa a ƙasar da ƙarin farashin mai ya haifar.

Kafofin yaɗa labarai sun ruwaito shugabannin ƙungiyar ma’aikata ta NLC da ta ‘yankasuwa TUC sun gana da wakilan gwamnatin tarayya a ofishin sakataren gwamnati da ke Abuja ranar Alhamis.

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris, ya shaida wa manema labarai a ƙarshen taron cewa taron alama ce da ke nuna yadda gwamnati ta mayar da hankali wajen tattaunawa da ƴan ƙwadago a kan batun.

Sai dai kuma ministan ya ƙi faɗar abubuwan da aka tattauna a wajen taron, yana mai cewa gwamnati ba za ta zura ido har sai abubuwa sun lalace ba sannan ta gana da ƙungiyoyin ƙwadagon.

“An tattauna abubuwa da dama amma kamar yadda na faɗa tun farko, har yanzu ana cikin sasanci ne, kuma wannan harka ce da ba za a iya gamawa a zama ɗaya ba, kuma kawo yanzu ba mu cim ma wani abu da za a iya faɗa wa ƴan Najeriya ba,” in ji shi.

Ƴan Najeriya da dama sun bayyana rashin jin daɗinsu kan ƙarin farashin man fetur da aka yi kwanan nan a ƙasar, da kuma tsadar rayuwa da ake fama da ita.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp