fidelitybank

Ba a cimma matsaya ba tsakanin Gwamnati da Kungiyoyin Kwadago

Date:

Ba a cim ma matsaya ba a taron tattaunawa tsakanin haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙwadago da gwamnatin Najeriya game da tsadar rayuwa a ƙasar da ƙarin farashin mai ya haifar.

Kafofin yaɗa labarai sun ruwaito shugabannin ƙungiyar ma’aikata ta NLC da ta ‘yankasuwa TUC sun gana da wakilan gwamnatin tarayya a ofishin sakataren gwamnati da ke Abuja ranar Alhamis.

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris, ya shaida wa manema labarai a ƙarshen taron cewa taron alama ce da ke nuna yadda gwamnati ta mayar da hankali wajen tattaunawa da ƴan ƙwadago a kan batun.

Sai dai kuma ministan ya ƙi faɗar abubuwan da aka tattauna a wajen taron, yana mai cewa gwamnati ba za ta zura ido har sai abubuwa sun lalace ba sannan ta gana da ƙungiyoyin ƙwadagon.

“An tattauna abubuwa da dama amma kamar yadda na faɗa tun farko, har yanzu ana cikin sasanci ne, kuma wannan harka ce da ba za a iya gamawa a zama ɗaya ba, kuma kawo yanzu ba mu cim ma wani abu da za a iya faɗa wa ƴan Najeriya ba,” in ji shi.

Ƴan Najeriya da dama sun bayyana rashin jin daɗinsu kan ƙarin farashin man fetur da aka yi kwanan nan a ƙasar, da kuma tsadar rayuwa da ake fama da ita.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp