fidelitybank

Ba a biyan haraji yadda ya kamata a Najeriya – Bill Gates

Date:

Hamshaƙin attajirin nan na Amurka, Bill Gates ya ce ba a karɓar haraji yadda ya kamata a Najeriya.

Yayain da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan abinci mai gina jiki da wata ƙungiyar matasan Afirka ta shirya a Abuja, shugaban gidauniyar Bill and Melinda Gates, ya ce nan da wani lokaci mai zuwa, Najeriya na iya zama babbar ƙasar da ke fitar da abinci zuwa kasuwannin duniya .

“A fannin noma, a yau Najeriya na ɗaya daga cikin manyan ƙasashen da ke sayo abinci daga ƙetare, amma duba da yawan jama’ar ƙasar idan ƙasar ta yi amfani da shawarwarin da ake bai wa manoman ƙasar, to akwai yiwuwar ƙasar za ta samu bunƙasa a fannin samar da abinci, ta yadda ma za ta zama babbar mai fitar a abinci a duniya”, in ji shi.

Hamshaƙain attajirin ya kuma ce ya kamata manoman ƙasar su rungumi hanyoyin noma na zamani tare da amfani da irin shuka mai inganci domin samun bunƙasar noman abinci a ƙasar.

Haka kuma ya yi kira ga gwamnatin ƙasar ta bunƙasa fannin lafiyarta.

“Ya kamata a bai wa fannin lafiya fifiko. Gwamnatin ƙasar ta jima tana yin shirin ɗaukar nauyin fannin lafiyar fiye da yadda yake a yanzu. To sai dai a haƙiƙanin gaskiya a Najeriya ba a biyan haraji yadda ya kamata”.

Bill Gates ya ce duk ‘yan ƙasar da ke son ilimi da lafiyarsu do ya wajaba a kansu su riƙa sauke haƙƙokin da ke kansu.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp