fidelitybank

Ba a biyan haraji yadda ya kamata a Najeriya – Bill Gates

Date:

Hamshaƙin attajirin nan na Amurka, Bill Gates ya ce ba a karɓar haraji yadda ya kamata a Najeriya.

Yayain da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan abinci mai gina jiki da wata ƙungiyar matasan Afirka ta shirya a Abuja, shugaban gidauniyar Bill and Melinda Gates, ya ce nan da wani lokaci mai zuwa, Najeriya na iya zama babbar ƙasar da ke fitar da abinci zuwa kasuwannin duniya .

“A fannin noma, a yau Najeriya na ɗaya daga cikin manyan ƙasashen da ke sayo abinci daga ƙetare, amma duba da yawan jama’ar ƙasar idan ƙasar ta yi amfani da shawarwarin da ake bai wa manoman ƙasar, to akwai yiwuwar ƙasar za ta samu bunƙasa a fannin samar da abinci, ta yadda ma za ta zama babbar mai fitar a abinci a duniya”, in ji shi.

Hamshaƙain attajirin ya kuma ce ya kamata manoman ƙasar su rungumi hanyoyin noma na zamani tare da amfani da irin shuka mai inganci domin samun bunƙasar noman abinci a ƙasar.

Haka kuma ya yi kira ga gwamnatin ƙasar ta bunƙasa fannin lafiyarta.

“Ya kamata a bai wa fannin lafiya fifiko. Gwamnatin ƙasar ta jima tana yin shirin ɗaukar nauyin fannin lafiyar fiye da yadda yake a yanzu. To sai dai a haƙiƙanin gaskiya a Najeriya ba a biyan haraji yadda ya kamata”.

Bill Gates ya ce duk ‘yan ƙasar da ke son ilimi da lafiyarsu do ya wajaba a kansu su riƙa sauke haƙƙokin da ke kansu.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp