Ofishin jakadancin Najeriya da ke birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar ya musanta rahotannin da ke cewa masu zanga-zanga sun ƙona ofishin.
Tun a tsakiyar mako aka fara yaɗa wani bidiyo a shafukan sada zumunta da iƙirarin cewa masu goyon bayan sojojin mulki a Nijar ɗin ne suka cinna wa ofishin wuta.
“Duk da cewa masu zanga-zanga sun so kutsawa cikinsa a ranar 30 ga watan Yuli, sojojin Nijar da ‘yan sanda sun daƙile yunƙurinsu,” a cewar wata sanarwa da ofishin ya fitar ranar Juma’a.
“Har yanzu sojojin Nijar da sauran jami’n tsaro na ci gaba gadin sa.”
Shugaban Najeriya Bola Tinubu, a matsayinsa na shugaban ƙungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Yamma (Ecowas), shi ne ke jagorantar yunƙurin matsa wa sojoji su mayar da Shugaba Bazoum Mohamed kan mulki.
Tuni ƙungiyar ta umarci hafsoshin tsaronta su shirya kutsa kai Nijar don tilasta wa sojojin sauka daga mulki. In ji BBC.