A na sa ran dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, zai dawo cikin makon nan.
Yana shirin jagorantar gangamin jam’iyyar na zaben gwamnan Osun a Osogbo ranar Alhamis.
Majiyoyi sun shaida wa LEADERSHIP cewa, a yau ne ake sa ran Atiku zai dawo Najeriya bayan ya shafe makonni a kasar waje.
Komawar tasa na zuwa ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa, gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike, zai sauya sheka, kan hanyar da aka yi masa na tsayawa takara.
Atiku ya zabi gwamnan jihar Delta, Sen Ifeanyi Okowa, a matsayin mataimakinsa bayan 14 daga cikin 17 na kwamitin ba da shawara suka rataya a wuyan Wike.
Ana sa ran zai jagoranci sulhun da Wike wanda a ranar Juma’a ya gana da gwamnonin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) guda uku, wato, Kayode Fayemi (Ekiti); Rotimi Akeredolu (Ondo) da Babajide Sanwoolu (Lagos), a gidansa na kashin kansa da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribas.