fidelitybank

Atiku ya zargi INEC da yunƙurin yin mafi a 2023

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya yi zargin cewa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na aza harsashin magudin zaben 2023 ta hanyar tattara sakamako da hannu.

Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye a wata hira da jaridar Punch a ranar Asabar ya ce, za a gudanar da tattara sakamakon zaben shekarar 2023 da hannu duk da amincewar da aka yi ta hanyar amfani da na’urar tantance sakamakon zabe.

An ruwaito Okoye yana cewa “Sashe na 60(5) na dokar ya zama wajibi shugaban hukumar ya mika sakamakon zaben da suka hada da jimillar adadin wadanda aka tantance da kuma sakamakon kuri’un ta hanyar da hukumar ta tsara. Bayan haka, shugaban hukumar bayan nadawa da bayyana sakamakon zai bayar da makamantan kayayyakin zabe a karkashin tsaro tare da rakiyar ’yan takara ko wakilansu, inda za a samu wanda hukumar ta tsara.

“Ma’anar wannan ita ce har yanzu tsarin tattara sakamakon na kan hannu ne, amma jami’in tattara sakamakon dole ne ya tattara sakamakon bincikensa tare da tabbatar da cewa adadin wadanda aka amince da su da aka bayyana kan sakamakon da aka tattara daidai ne kuma sun yi daidai da adadin wadanda aka amince da su. Ya kara da cewa an rubuta kuma ana yada shi kai tsaye daga rumfunan zabe.

Atiku, wanda ya ke mayar da martani ta bakin mai magana da yawunsa, Daniel Bwala Sunday, ya yi zargin cewa, da irin wannan furucin “INEC na aza harsashin magudin zaben 2023”.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp