fidelitybank

Atiku ya yi tir da kisan gillar da ‘yan bindiga su ka yi a Katsina

Date:

Ɗan takarar shugaban jam’iyyar adawa ta PDP, a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, ya yi alla-wadai da harin da aka kai ƙauyen Ƴargoje da ke jihar Katsina, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Harin da ‘yan bindiga suka kai, ya kuma haɗa da garkuwa da mata da kananan yara marasa galihu, lamarin da ya kara ta’azzara wa al’ummar yankin.

Da yake nuna alhininsa game da faruwar lamarin, Atiku ya yi ƙarin haske kan harin kwantan ɓauna da maharan suka yi wa jami’an tsaron da ke amsa kiran gaggawa a kauyukan Gidan Tofa da Dan Nakwabo wanda yayi sanadin mutuwar jami’an ‘yan sanda hudu da wasu ‘yan kungiyar sa ido na jihar Katsina guda biyu.

“Wannan babban rashi ne, kuma tunanina yana tare da iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu,” in ji shi

Atiku ya soki matakan da gwamnati ke dauka kan matsalar tsaro da ake fama da ita, inda ya nuna cewa ayyukan ‘yan fashi da ta’addanci sun zama ruwan dare gama gari.

Ya bayyana damuwarsa kan gazawar gwamnati da kuma rashin ɗaukar ƙwararan matakai, duk da gagarumin kasafin kudin shekara da ake warewa tsaro.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi kira ga gwamnati da ta kara daukar nauyinta na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa da muhimmanci.

Ya bukaci da a dauki kwararan matakai na yaƙi da matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a yankin.

“Ya kamata lafiyar al’ummarmu ta kasance a gaba, kuma dole ne gwamnati ta kara himma wajen tabbatar da hakan,” in ji Atiku

Atiku ya kuma bayyana juyayinsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, inda ya bukace su da su kara kaimi a wannan mawuyacin lokaci.

A ranar Lahadin da ta gabata ne mazauna garin Yargoje suka faɗa wa kamfanin labarai na Reuters cewa maharan sun afka wa ƙauyen tun da dare inda aƙalla mutum 50 aka kashe sannan aka sace wasu da ba a san adadinsu.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp