fidelitybank

Atiku ya yi fata-fata da Tinubu kan karin man fetur

Date:

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya caccaki shugaban Najeriya, Bola Tinubu kan abin da ya kira gazawarsa wajen tafiyar da sha’anin makamashi.

Atiku Abubakar wanda ya yi takara da Tinubu a zaɓen 2023, ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis cewa gwamnatin Tinubu ta lalata al’amura da sunan cire tallafin mai.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar, ya danganta matsalolin da ƴan Najeriya ke fuskanta da irin tsarin gwamnatin Tinubu na “ta ci barkatai” kan yadda take tafiyar da sha’anin makamashi.

Atiku ya kuma bayyana damuwa kan ƙamarin da hauhawar farashi ya yi a ƙasar inda ya ce al’amarin da matuƙar ƙuntata wa ƴan Najeriya.

“Riƙon sakainar kashi da wannan gwamnatin ke yi wa tsarin cire tallafin mai shi ne babban dalilin da ya sa muke cikin yanayin ƙunci da muke ciki a ƙasar nan.

“A yanzu haka, babu wani fata dangane da hauhawar farashin kaya wanda ya karya ƙarfin tattalin arziƙin ƴan Najeriya.

“Abin takaici ma shi ne yadda al’amarin ba ya damun T-pain,” Kamar yadda Atiku ya rubuta.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp