fidelitybank

Atiku ya shigar da karar Tinubu a kotun Amurka

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, Atiku Abubakar, ya shigar da wata sabuwar kara a gaban kotun kasar Amurka da ke yankin Arewacin jihar Illinois a kasar Amurka, kan shugaban kasa Bola Tinubu bayan ya janye karar da ake yi a baya.

Ku tuna cewa kotun karamar hukumar da ke jihar Illinois ta yi watsi da karar da Atiku ya shigar, yana neman a saki bayanan karatun Tinubu a Jami’ar Jihar Chicago.

Atiku ya kai karar Jami’ar Jihar Chicago (wanda ake kara) gaban kotu, inda ya nemi a ba shi umarnin tilasta wanda ake kara ya saki bayanan karatun Tinubu a hannunta.

Sai dai a cewar Phrank Shaibu, mataimaki na musamman kan hulda da jama’a ga Atiku, korar ta biyo bayan janye karar da shugaban makarantar ya yi.

Arisenews ta ruwaito Shaibu ya bayyana haka ne a ranar Lahadin da ta gabata yayin da yake mayar da martani game da korar karar da kotun da’ar yankin Cook ta yi.

Shaibu ya ce, “Waziri Atiku Abubakar ya janye karar ne kawai a gaban wata kotun da’ar da ke gundumar Cook da ke gundumar Illinois ta Amurka, saboda yana gudanar da irin wannan lamari a wata babbar kotu kuma yana so ya kaucewa cin zarafin kotu. Don haka, wannan mafari ne kawai.”

Ya kara da cewa abin dariya ne yadda Tinubu da magoya bayansa suka yi murna da wannan ci gaba kamar dai hukuncin kotun koli ne.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ĉ´ansandan jihar Kaduna, sun buĈ™aci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi Ĉ™ungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban Ĉ™aramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp