Dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ziyarci Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, domin neman goyon bayan wakilan jam’iyyar gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a ranar 28 ga watan Mayu.
Atiku Abubakar ya gana da shugabannin jam’iyyar PDP da suka hada da ‘yar takarar gwamna Ladi Adebutu, da shugaban jam’iyyar na jihar, Sikirullahi Ogundele, a sakatariyar jam’iyyar ta jihar.
Yayin da yake zayyana kuri’un wakilan, Atiku Abubakar ya ce, ya fi cancantar wakilci jam’iyyar da kuma mulkin kasa bisa kwarewa.
Ya bayyana cewa, idan aka zabe shi a kan karagar mulki, zai gudanar da mulkin Najeriya ne a kan wasu manifofi guda biyar, wato hadin kai, tsaro, tattalin arziki, ilimi da kuma ba da karin albarkatu da madafun iko ga sassan tarayya.
“Na yi alkawarin baiwa kowane bangare na kasar nan fahimtar zama kamar yadda muka yi a baya.
“Lokacin da muka hau mulki a 1999, mun fuskanci rashin hadin kai, kuma abu na farko da muka yi shi ne kafa gwamnatin hadin kan kasa wanda ya samar da zaman lafiya da muke bukata domin samun nasarar gudanar da mulki,” in ji shi.
Dan takarar ya sha alwashin magance matsalar rashin tsaro a fadin Najeriya, inda ya bayyana cewa hakan ne tushen ci gaban tattalin arzikin kasar.