fidelitybank

Atiku ya na da ƙwarewar da zai jagoranci Najeriya – Ƙungiya

Date:

Kungiyar mambobin Jam’iyyar PDP daga yankin Kudu maso Kudu da aka yiwa lakabi da kungiyar yakin neman zabe ta KARADE-MAZABU karkashin jagorancin Ada Fredrick Okwori, sun ziyarci  Atiku Abubakar a gidan sa dake Abuja.

Da yake magana a yayin ganawar, daya Daga cikin ayarin Honorable Omoge Tamuno, ya ce, kungiyar tasu tana da yakinin cewar tsohon mataimakin shugaban kasar nada kwarewar da ake Bukata wajen tafiyar da mulkin kasar nan, kuma zai iya kubatar da ita daga halin da ta ke ciki sannan ya sake dora ta kan tafarkin zaman lafiya da haɗin kai, yana mai cewar Atiku yana cikin mutanen da suka farfado da tattalin arzikin kasar nan a baya.

Haka kuma, wani mamban ayarin ya bayyana Wazirin Adamawa a matsayin mutum wanda ya bada muhimmiyar gudummawa wajen bunkasar dimukuradiyya a Najeriya.

Mambobin ayarin sun kada kuri’ar goyon baya ga dan takarar shugaban kasar na PDP a zaben na 2023, inda ya ce sun yi kyakkyawan shiri domin samarwa Atiku Abubakar cikakken goyan baya Daga tushe.

Sanarwar da hadimin Atiku a kafafen yaɗa labarai, Abdulrasheed Shehu ya aikewa manema labarai ya ce, a nasa bangaren, dan takarar shugabancin na Najeriya ya yi marhabin da bakin, kuma ya gode musu bisa ziyarar, inda ya bukace su da jajircewa Wajen aiki domin nasarar Jam’iyyar PDP a zaben badi don kyakkyawar makoma ga Najeriya.

Mataimaki na Musamman ga Mai girma Atiku Abubakar kan kafafen yada labarai.

10 ga watan Agusta 2022.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp