fidelitybank

Atiku ya mika tallafin Naira miliyan 50 zuwa Katsina

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 50 ga wadanda ‘yan fashin daji suka shafa a jihar Katsina.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya sanar da bayar da tallafin ne a ranar Talata a lokacin da ya kai gaisuwar ban girma ga mai martaba Sarkin Katsina, Dr. Abdulmumini Kabir Usman a fadarsa da ke Katsina, babban birnin jihar.

Atiku wanda ke Katsina a ci gaba da yakin neman zabensa na 2023, ya samu rakiyar abokin takararsa kuma gwamnan jihar Delta, Dokta Ifeanyi Okowa; shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Iyorchia Ayu; Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal; Tsohon Gwamnonin Neja, Kano, Jigawa da Kaduna, Aliyu Babangida, Ibrahim Shekarau, Sule Lamido, Ahmed Maikarfi, da sauransu zuwa fadar sarki.

Ya jajanta wa al’ummar Katsina da sauran jihohin Arewa kan matsalar rashin tsaro da sauran kalubalen da ke addabar yankin.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya sha alwashin kawar da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke addabar yankin idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasar a babban zabe mai zuwa na 2023.

Ya ce: “Ina jajanta wa al’ummar Katsina da sauran jihohin Arewa da ke fuskantar kalubalen tsaro da tattalin arziki. Ina so in tabbatar muku da cewa idan aka zabe ni a matsayin shugaban Najeriya, zan kawo karshen wadannan kalubale.

“A madadina, ina bayar da gudummawar Naira miliyan 50 ga wadanda rikicin ‘yan bindiga ya shafa a jihar da suka koma wasu wurare a sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a cikin al’ummarsu.”

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp