fidelitybank

Atiku ya mika tallafin Naira miliyan 50 zuwa Katsina

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 50 ga wadanda ‘yan fashin daji suka shafa a jihar Katsina.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya sanar da bayar da tallafin ne a ranar Talata a lokacin da ya kai gaisuwar ban girma ga mai martaba Sarkin Katsina, Dr. Abdulmumini Kabir Usman a fadarsa da ke Katsina, babban birnin jihar.

Atiku wanda ke Katsina a ci gaba da yakin neman zabensa na 2023, ya samu rakiyar abokin takararsa kuma gwamnan jihar Delta, Dokta Ifeanyi Okowa; shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Iyorchia Ayu; Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal; Tsohon Gwamnonin Neja, Kano, Jigawa da Kaduna, Aliyu Babangida, Ibrahim Shekarau, Sule Lamido, Ahmed Maikarfi, da sauransu zuwa fadar sarki.

Ya jajanta wa al’ummar Katsina da sauran jihohin Arewa kan matsalar rashin tsaro da sauran kalubalen da ke addabar yankin.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya sha alwashin kawar da matsalolin tsaro da tattalin arziki da ke addabar yankin idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasar a babban zabe mai zuwa na 2023.

Ya ce: “Ina jajanta wa al’ummar Katsina da sauran jihohin Arewa da ke fuskantar kalubalen tsaro da tattalin arziki. Ina so in tabbatar muku da cewa idan aka zabe ni a matsayin shugaban Najeriya, zan kawo karshen wadannan kalubale.

“A madadina, ina bayar da gudummawar Naira miliyan 50 ga wadanda rikicin ‘yan bindiga ya shafa a jihar da suka koma wasu wurare a sakamakon hare-haren ‘yan bindiga a cikin al’ummarsu.”

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp