fidelitybank

Atiku ya magantu a kan zaben Imo da Kogi tare da Bayelsa

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya yi kira ga dukkanin kungiyoyin da ke goyon bayan sa da su tashi tsaye domin samun nasarar jam’iyyar a zaben gwamna a jihohin Bayelsa, Kogi da kuma Imo.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta tsayar da ranar 11 ga watan Nuwamba domin gudanar da zaben gwamna a jihohin Bayelsa, Imo da Kogi.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar goyon bayan Atiku Abubakar, Oladimeji Fabiyi ya fitar a ranar Litinin, Atiku ya jaddada matukar bukatar lashe jihohin kasar nan zuwa PDP.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mai Girma Atiku Abubakar (Wazirin Adamawa) GCON ya umurci dukkanin kungiyoyin goyon bayan Atiku da ke da manyan tsare-tsare a jihohin Kogi, Bayelsa da Imo da su tashi tsaye wajen zaburar da mambobinsu domin marawa jam’iyyar PDP a wadannan jihohin.

“Mambobi su tabbatar da cewa sun jajirce wajen zaben ‘yan takarar jam’iyyar, Mai Girma, Sanata Duoye Diri na Jihar Bayelsa, Sanata Sam Anyanwu (Sam Daddy) na Jihar Imo da Sanata Dino Daniel Melaye na Jihar Kogi.

“Mai girma Atiku Abubakar ya kuma jaddada matukar bukatar lashe wadannan jahohin ga jam’iyyar PDP. Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa dukkan masu rike da tuta na PDP guda uku suna da hangen nesa, gogewar da ake bukata, da damar jagorantar PDP a zabe mai zuwa.”

Fabiyi ya bayyana cewa, tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce ko shakka babu jam’iyyar PDP ta gabatar da jiga-jigan ‘yan takara masu karfin hali, gogewa da kuma iya shugabancin jihar.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp