Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, a ranar Laraba a Katsina, ya yi alkawarin dawo da hadin kan Najeriya, idan aka zabe shi shugaban kasa a 2023.
Atiku ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da yake jawabi ga wakilai da shugabannin jam’iyyar PDP reshen jihar Katsina a sakatariyar jam’iyyar da ke Katsina.
Tsohon mataimakin shugaban kasa ya lura cewa, hadin kan Najeriya wanda ya zama ginshikin kafa jam’iyyar PDP wanda kuma ya sanya jam’iyyar ta ci gaba da rike hadin kan kabilu daban-daban da suka hada da Najeriya, jam’iyyar All Progressives Congress ta ruguje.
Sai dai ya shaida wa ‘yan jam’iyyar PDP cewa, idan aka zabe shi a matsayin shugaban Najeriya zai dawo da hadin kai tare da gyara duk wasu illolin da jam’iyyar APC ta jefa kasar nan.