Peter Olagookun, shugaban jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a jihar Ondo, ya jaddada cewa nasarar da jam’iyyar adawa ta shirya ta yi ya ta’allaka ne kan hadin kan manyan ‘yan jam’iyyar.
Ya yi imanin cewa ta hanyar hadin kai ne kawai za a iya kalubalantar jamâiyya mai mulki a zaben 2027.
A wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) a ranar Alhamis a birnin Akure, Olagookun ya bayyana cewa ya kamata tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya yi tunanin komawa gefe don bai wa Rabiu Kwankwaso damar tsayawa takarar shugaban kasa a jamâiyyar adawa a 2027.
Kwankwaso, Abubakar, da Peter Obi sun kasance âyan takarar shugaban kasa na jamâiyyun NNPP, PDP, da Labour Party (LP) a zaben 2023, bi da bi.
Duk âyan takarar uku Bola Tinubu na jamâiyyar APC ne ya kayar da su.
Tun bayan zaben dai ake ta rade-radin cewa akwai yuwuwar kawance tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa uku na kalubalantar Tinubu a 2027, duk da cewa Kwankwaso ya musanta wadannan ikirari.
A ranar 20 ga watan Maris, Atiku ya tabbatar da cewa shi da sauran âyan adawa za su kafa kawance don karbe mulki daga hannun jamâiyya mai mulki a shekarar 2027.
Olagookun ya bukaci shugabannin âyan adawa da su yi watsi da burin kashin kansu su marawa Kwankwaso baya a matsayin dan takarar shugaban kasa a zaben 2027.
“Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, Alhaji Atiku Abubakar, Mista Peter Obi, Malam Nasir El-Rufai, da sauran masu fafutukar kafa kawancen ‘yan adawa su sa Atiku ya fice daga takarar shugaban kasa a 2027,” in ji Olagookun.
âYa kamata ya marawa abokin aikinsa Kwankwaso baya, sannan kuma su zabi dan takara mai karfi daga Kudu a matsayin abokin takararsa, na yi imanin cewa da wannan tsari jamâiyya mai mulki za ta yi gwagwarmayar tinkarar âyan adawaâ.
Sai dai Olagookun ya yi gargadin cewa idan ba tare da wannan matakin hadin kai ba, kungiyar za ta yi kasa a gwiwa kuma za ta wargaje kafin zaben 2027.
Ya kara da cewa “Idan Atiku ya koma gefe, tarihi zai gane rashin son kai da kishin kasa.” âKwankwaso sahihin dan takara ne wanda zai iya jagorantar âyan adawa ga nasara a 2027.â
Olagookun ya kuma yabawa Atiku bisa kokarinsa na hada kan shugabannin adawa da kuma irin gudunmawar da yake bayarwa wajen ci gaban kasa.