Kungiyar Peter Obi Support Network, ta roki tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar da ya janye aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023 tare da hada dabarun siyasarsa, domin marawa burin tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi na tsayawa takarar shugaban kasa.
Kungiyar goyon bayan a wata wasika mai dauke da kwanan watan 19 ga watan Afrilu wacce aka mika wa ofishin Atiku a ranar 20 ga watan Afrilu, ta ce watsi da bukatar shugaban kasa da Alhaji Atiku ya yi na samar da daidaito, adalci.
Kungiyar a cikin wasikar ta bayyana cewa, ya sabawa ka’idar adalci, daidaito da kuma adalci ga wani dan takara daga Arewacin Najeriya ya yi yakin neman shugabancin kasa bayan shugaban kasa Muhammadu Buhari na shekaru takwas a kan karagar mulki nan da 2023.
Sanarwar ta kara da cewa, “Muna rubuto a madadin miliyoyin ‘ya’yanmu a fadin Najeriya, domin mu yi kira gare ka, Shugaban Jam’iyyarmu, H.E Alhaji Atiku Abubakar (GCON), da ka yi amfani da wannan lokaci, ka kuma sake nuna irin shugabancin da ka iya nunawa a 2019.Â
“Tikitin Atiku/Obi na 2019 ya shiga tarihi a matsayin tikitin takarar shugaban kasa a Najeriya da ya fi daukar hankali a kowane lokaci, wanda a ganinmu an ki cin nasara ba bisa ka’ida ba.