fidelitybank

Atiku ya janye daga duba kayan zaben INEC

Date:

Ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam’iyyar, PDP, Atiku Abubakar, shi da jam’iyyarsa sun janye sabuwar ƙarar da suka shigar ta neman tilasta wa hukumar zaɓe ba su damar duba kayan da aka yi amfani da su a zaɓen ranar 25 ga watan Fabarairu.

Atikun da jam’iyyarsa da ke ƙalubalantar sakamakon zaɓen da aka ayyana Bola Ahmed Tinubu na jam’iyya mai mulki APC a matsayin wanda ya ci zaɓen, sun shaida wa kotun musamman da ke sauraren ƙararraki kan zaɓen shugaban ƙasar a Abuja cewa ba su da buƙatar ci gaba da ƙarar.

Jagoran ayarin lauyoyin da ke wakiltar Atikun da PDP Mista Joe-Kyari Gadzama (SAN) shi ne ya shaida wa kotun haka lokacin da aka zauna fara sauraren ƙarar a yau Laraba.

Karanta Wannan: Wike ya caccaki Amaechi akan zabar Atiku maimakon Obi

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa wani daga cikin lauyoyin na Atiku da PDP, wanda bai yarda a ambaci sunansa ba, ya ce tun da farko sun shigar da ƙarar ne saboda matsaloli da ƙalubalen da suka gamu da su lokacin da wakilan jam’iyyar da Atiku suka je hukumar zaɓen domin a ba su kayan su duba, kamar yadda kotu ta bayar da umarni.

Ya ce, to kasancewar kafin a zo sauraren wannan ƙara da suka shigar ta tilasta wa INEC barin wakilan su duba kayan zaɓen, INEC da kanta ta fito ta yi alƙawarin ba su damar su je su duba wasu daga cikin kayan musamman ma takardar da aka yi zaɓe, ya ce saboda haka ne suka janye wannan sabuwar ƙara.

Atiku da jam’iyyar tasa da kuma ɗan takarar Labour shi ma da jam’iyyar tasa dukkaninsu suna ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasar na Najeriya, inda kowanne daga cikin ɓangaororin biyu ke iƙirarin shi ne ya yi nasara aka yi masa fashi, tare da lasar takobin ƙwato nasarar tasu a kotu.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp