fidelitybank

Atiku ya gaza cika sharuɗan cin zaɓe – INEC

Date:

Hukumar zaɓe Mai Zaman Kanta INEC, ta ce, ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya gaza cika sharuɗɗan da tsarin mulkin ƙasa ya gindaya kafin a ayyana shi matsayin wanda ya lashe zaɓen ranar 25 ga watan Fabrairu.

INEC ta bayyana haka ne a matsayin martani kan ƙorafe-ƙorafen da ɗan takarar ya shigar gaban kotun sauraron ƙararrakin zaɓe.

Ta dai buƙaci kotun ta yi watsi da ƙorafin da ɗan takarar ya shigar gabanta yana ƙalubalantar sakamakon zaɓen da ya bai wa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC nasara.

Karanta Wannan: Majalisa ta gayyaci Ministan kuɗi a kan ɓatan kuɗaɗen man fetur

Hukumar ta ce Atiku ya gaza samun kashi 25 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa a aƙalla kashi biyu cikin uku na jihohin ƙasar 36 da kuma birnin tarayya Abuja, wanda hakan na cikin sharuɗɗan cin zaɓe a ƙasar.

Game da ƙorafin saɓa dokar zaɓe, INEC ta ce an gudanar da zaɓen ne bisa dokar zaɓen ƙasar ta 2022, ba tare da almundahana ba, kamar yadda masu ƙorafin suke zargi.

Hukumar zaɓen ta sake jaddada cewa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC shi ne halastaccen zaɓaɓɓen shugaban ƙasar.

Game da ƙorafin rashin samun rinjayen ƙuri’u a Abuja da ake yi wa Tinubu, INEC ta ce kundin mulkin Najeriya bai fitar da wani matsayi na musamman a kan ƙuri’un babban birnin ƙasar ba.

Domin haka, a cewarta ƙuri’un Abuja daidai suke da ƙuri’un kowacce jiha ta fuskar matsayi.

Atiku Abubakar tare da jam’iyyarsa ta PDP sun garzaya kotun ƙorafe-ƙorafen zaɓe ne domin ƙalubalantar sakamakon da ya bai wa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC nasara.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp