Tsohon dan majalisar dokokin Kogi ta tsakiya, Sanata Dino Melaye, ya bayyana cewa, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya fi koshin lafiya da gogewa a cikin dukkan ‘yan takarar shugaban kasa a 2023.
Melaye ya bayyana hakan ne a wajen taron bai wa Atiku da bikin kaddamar da ‘yan matan Diamond a harkokin siyasa da aka gudanar a yammacin ranar Asabar a Abuja, babban birnin kasar.
Ya kara da cewa, babu wani dalili na kwatanta Atiku da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, Bola Ahmed Tinubu.
Melaye ya ci gaba da cewa, magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP na gaskiya ne, kuma hamshakin attajirin ne da Atiku ya ke da sana’a.