fidelitybank

Atiku kar ka sake tsayawa takara a 2027 – Kungiyar Matasan PDP

Date:

Wata kungiya matsa a cikin jam’iyyar PDP, wato Concerned PDP League, CPDPL, ta yi kira ga Alhaji Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben shugaban kasa na 2023, da kada ya sake tsayawa takara a 2027.

Shawarar kungiyar na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka sanya wa hannu a ranar Lahadi kuma aka fitar a Abuja ta hannun sakatarenta na kasa, Alhaji Tasiu Muhammed da kuma mukaddashin daraktan yada labarai da sadarwa na kasa, Gbenga Adedamola.

CPDPL ta kuma bukaci shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, da kada ya sanya wani buri na neman kujerar shugaban kasa har sai 2031, don kaucewa sake afkuwar abin da ya faru da jam’iyyar a 2015 da 2023.

A cewar kungiyar, shawarar da ta bayar ya kasance masu sha’awar tsayawa takara daga Arewa su fahimci cewa Kudu tana da sauran shekaru takwas kafin mulki ya dawo Arewa a 2031.

“Shawarar mu kuma ita ce tabbatar da kwanciyar hankali a tsarin siyasar kasar,” in ji kungiyar.

Ta kuma shawarci jam’iyyar da ta yi taka-tsan-tsan da abubuwan da suka haddasa faduwarta a babban zaben 2023, tare da kauce musu yayin da take shirin tunkarar zaben 2027.

“Kamar yadda muka sani, shekarar 2023 shekara ce mai matukar kalubale ga babbar jam’iyyarmu, inda muka fadi zaben shugaban kasa saboda rashin bin kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu na 2017, kamar yadda aka yi wa kwaskwarima, da gazawar shugabanci,” in ji CPDPL.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp