Wata kungiyar Kudu maso Yamma ta shawarci tsohon shugaban kasar nan, Atiku Abubakar, cewa da ya hakura da batun tsayawar sa takara a zaben 2023 da ke karatowa.
A cewar jigon kungiyar, Olufemi Osabinu, ba zai yi wu dan Arewa ya ci gaba da mulkar kasar nan ba, bayan shugaba Buhari ya kammala shekaru 8 a mulki.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, yadda kungiyar South-West Development Frontier (SDF), ta mika wannan bukatar gare shi a ranar Litinin, 14 ga watan Fabrairu, inda ta ce Arewa ba za ta ci gaba da mulkin kasa ba, bayan Shugaba Muhammadu Buhari ya kammala shekaru 8 a kujerar mulki.
Olufemi Osabinu, jagoran kungiyar ya ce Atiku ya yi wa kasa aiki a baya, domin haka ya kamata ya baiwa yara masu jini a jika damar shugabanci, domin kawo karshen rashin tsaron da ke addabar kasar nan.