fidelitybank

Atiku da Wike: Jami’an tsaro sun rufe wuraren kasuwanci mallakin magoya bayan Atiku a Ribas

Date:

Dambaruwa a cikin jam’iyyar PDP a jihar Ribas na daukar wani sabon salo.

Na baya-bayan nan dai shi ne rufe wani gidan mai a Fatakwal da aka ruwaito mallakin dan majalisar wakilai, Chinyere Igwe.

Igwe dai na hannun damar tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai, Austin Opara, wanda ke goyon bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Haka kuma wani otal da aka ce mallakar Ikenda Chinda, dan uwan ​​Austin Opara ne kuma an kulle shi.

Hakazalika, wani dakin shakatawa na Ogbonda Jones, wanda kuma abokin Opara ne, shi ma ‘yan sanda sun rufe.

Ba a bayar da dalilin daukar matakin na ‘yan sandan ba.

Amma Igwe, yayin da yake mayar da martani game da ci gaban a ranar Juma’a, ya ce, matakin da hukumomin tsaro suka dauka a gidan man sa “siyasa ce”.

Wannan sabon al’amari dai na zuwa ne makonni biyu bayan da Gwamna Nyesom Wike ya yi barazanar rufe otal-otal da wuraren shakatawa da ke ba da wuraren da suke gudanar da taron siyasa na wadanda ya zarga da yunkurin tada zaune tsaye a jihar.

Yayin da rundunar ‘yan sandan jihar Ribas ba ta yi magana kan lamarin ba, alamu sun nuna cewa jami’an ‘yan sandan da suka aiwatar da wannan mataki sun fito ne daga gidan gwamnatin jihar Ribas. A cewar Daily Post.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp