Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Tinubu da Shettima, Festus Keyamo, ya yi ikirarin cewa, babu wani fata ga jamâiyyar PDP a zabe mai zuwa.
Bayanin hakan na kunshe ne a wani sako da ya wallafa ta shafin sa na Twitter da aka tabbatar.
Keyamo ya kuma yi zargin cewa, yakin neman zaben shugaban kasa na PDP ba zai kai labari ba, ya kara da cewa jamâiyyar na ciyar da magoya bayanta karya.
Gwamnonin APC ba za su taÉa goyon bayan Atiku ba – Bagudu
Ya rubuta cewa, âNa ji tausayin wasu da ke magana da yawun PDP; bayan rugujewar yakin neman zabensu da kuma adadin da bai karu ba, fatan da suke yi wa jamaâarsu shi ne karyar cewa Gwamnonin APC suna yi wa Atiku aiki a asirce. Ba tare da jingina ga APC ba, ba fata a gare su! Chai!!”