fidelitybank

ASUU za ta gana da gwamnati kan shiga sabon yajin aiki

Date:

Shugabannin kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, da gwamnatin tarayya za su yi taron ganawa a ranar Litinin, domin shawo kan bukatun malaman jami’o’in tare da dakile yajin aikin da ke tafe.

A ranar Larabar da ta gabata ne kungiyar kwadagon ta fitar da sanarwar yajin aikin kwanaki 21 ga gwamnati inda ta bukaci gwamnatin shugaba Bola Tinubu da ta magance duk wasu matsalolin da ba a warware ba da ke kawo cikas ga ci gaban jami’o’in Najeriya.

Farfesa Emmanuel Osodeke, shugaban kungiyar ASUU na kasa ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gudanar a jami’ar aikin gona ta Michael Okpara da ke Umudike a jihar Abia.

A wani yunkuri na dakatar da yajin aikin da ya kunno kai, Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman ya ce jami’an gwamnati za su gana da shugabannin kungiyar ASUU ranar Litinin.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis lokacin da ya bayyana a shirin bayan kwana 100 da aka watsa a TVC ranar Alhamis.

“Mun riga mun aika sanarwa ga shugabannin ASUU domin mu hadu a ranar Litinin.

“A ranar Laraba, mu (bangaren gwamnati) mun duba wasikar da ASUU ta mika da kuma dukkan batutuwan da ke cikin wasikar. Fatanmu shine zuwa ranar litinin mu hadu a tattauna dasu.

“Wasu daga cikin batutuwan na tarihi ne; lokacin da kake magana game da yarjejeniyar 2009. Wannan wani abu ne wanda ya samo asali tun kusan 1981 lokacin da suka fara.

“Mun jima muna tattaunawa da shugabannin kungiyar ASUU kan al’amuran da suka shafi tsarin jami’o’in domin mu, tare, mu magance dukkan matsalolinsu,” inji shi.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp