Shugabannin kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, da gwamnatin tarayya za su yi taron ganawa a ranar Litinin, domin shawo kan bukatun malaman jami’o’in tare da dakile yajin aikin da ke tafe.
A ranar Larabar da ta gabata ne kungiyar kwadagon ta fitar da sanarwar yajin aikin kwanaki 21 ga gwamnati inda ta bukaci gwamnatin shugaba Bola Tinubu da ta magance duk wasu matsalolin da ba a warware ba da ke kawo cikas ga ci gaban jami’o’in Najeriya.
Farfesa Emmanuel Osodeke, shugaban kungiyar ASUU na kasa ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gudanar a jami’ar aikin gona ta Michael Okpara da ke Umudike a jihar Abia.
A wani yunkuri na dakatar da yajin aikin da ya kunno kai, Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman ya ce jami’an gwamnati za su gana da shugabannin kungiyar ASUU ranar Litinin.
Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis lokacin da ya bayyana a shirin bayan kwana 100 da aka watsa a TVC ranar Alhamis.
“Mun riga mun aika sanarwa ga shugabannin ASUU domin mu hadu a ranar Litinin.
“A ranar Laraba, mu (bangaren gwamnati) mun duba wasikar da ASUU ta mika da kuma dukkan batutuwan da ke cikin wasikar. Fatanmu shine zuwa ranar litinin mu hadu a tattauna dasu.
“Wasu daga cikin batutuwan na tarihi ne; lokacin da kake magana game da yarjejeniyar 2009. Wannan wani abu ne wanda ya samo asali tun kusan 1981 lokacin da suka fara.
“Mun jima muna tattaunawa da shugabannin kungiyar ASUU kan al’amuran da suka shafi tsarin jami’o’in domin mu, tare, mu magance dukkan matsalolinsu,” inji shi.