fidelitybank

ASUU ta ƙara tsawaita mako huɗu na yaƙin aiki

Date:

Kungiyar Malaman Jami’o’i a Najeriya ta ASUU ta bayyana matakin tsawaita yajin aikin da take yi da mako hudu.

A cewar rahoton BBC, dama ASUU ta shafe sama da watanni biyar tana yajin aikin bayan gaza cimma matsaya da gwamnatin Najeriya, yanzu kuma gashi ta kara wata daya.

Idan har aka shafe wasu makonni hudu ba a sasanta tsakanin gwamnati da ASUU ba, hakan na nufin ɗaliban jami’o’in sun shafe rabin shekara suna zaman jiran tsammani a gida.

Sanarwar da ASUU ta fitar na dauke da sa hannun Shugaban kungiyar Emmanuel Osodeke, an kuma fitar da ita ne bayan kammala wani zaman gaggaawa na jiga-jigan kungiyar ranar Lahadi a Abuja.

Hakama ASUU ta gode wa ƙungiyar Kwadago ta NLC, da sauran kungiyoyin da suka mara mata baya wurin yin zanga-zangar nuna goyon baya da nufin kawo karshen yajin aikin.

Kungiyar Malaman Jami’ar ta kara da cewa ta tsawaita yajin aikin ne da mako hudu, lura da cewa har yanzu gwamnatin Najeriya ba ta nuna wata alama ta kawo karshen zaman daliban a gida ba.

Tun a ranar 14 ga watan Fabrairu ne ASUU ta tsunduma yajin aiki, bisa zargin gwamnatin Najeriya da gaza cika alkawuran da ta dauka a yarjejeniyar da suka ƙulla, ciki har da batun inganta rayuwar malaman da kuma dambarwar shigar da kungiyar tsarin biyan albashi na IPPIS da gwamnatin ta fito da shi.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp