fidelitybank

ASUU ta umarci Malaman Jos su zauna a gida saboda albashi

Date:

Reshen Jami’ar Gwamnatin Tarayya ta Jos na ƙungiyar malaman jami’a ta ASUU ta umarci mambobinta su zauna a gida har sai gwamnati ta biya su albashinsu da ta riƙe.

Rahotanni sun ambato shugaban ASUU a jami’ar, Dr Lazarus Maigoro, yana faɗar haka cikin wata sanarwar da ya fitar a garin na Jos ranar Juma’a.

Sai dai Maigoro ya ce ba yajin aiki suka shiga ba amma dai an ɗauki matakin ne bayan taron da suka gudanar a ranar Juma’ar sakamakon ƙin biyan su cikakken albashin da gwamnati ta yi na watan Oktoba.

Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ɓangarorin yarjejeniyar da suka cimma da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Femi Gbajabeamila shi ne gwamnati za ta biya kashi 50 cikin 100 na albashin watannin da ta riƙe musu nan take.

“Yanzu da muke magana, albashin kwana 17 kawai aka biya mu na watan Oktoba daga ofishin akanta janar na ƙasa,” a cewarsa.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp