fidelitybank

ASUU ta tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani – Farfesa Emmanuel

Date:

Kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta ayyana yajin aikin sai baba-ta-gani.

Hakan ya fito ne a wata sanarwa da shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ya sanya wa hannu.

Ya ce, kungiyar ta lura da takaicin yadda kungiyar ta fuskanci yaudara mai yawa a mataki mafi girma a cikin shekaru biyar da rabi da suka gabata, inda ya ce gwamnatin tarayya ta tsunduma ASUU a tattaunawar da ba ta da tushe ba tare da nuna rikon amana ba.

“Saboda abubuwan da aka yi a baya, da kuma bayan tattaunawa mai zurfi kan martanin da gwamnati ta mayar kan kudurin ranar 14 ga watan Fabrairun 2022, ya zuwa yanzu, NEC ta kammala da cewa ba a yi nasarar magance bukatun kungiyar ba.

“Saboda haka, NEC ta yanke shawarar sauya yajin aikin zuwa cikakken yajin aikin da zai fara daga karfe 12.01 na safe Litinin 29 ga Agusta, 2022,” sanarwar ta kara da wani bangare.

Ya kara da cewa: “NEC ta amince da kokarin da fitattun ‘yan Najeriya da kungiyoyi ke yi a baya da kuma na yanzu don shiga tsakani a rikicin da ya kunno kai. Ƙungiyarmu ta kasance a buɗe don yin aiki mai ma’ana kamar yadda muka saba yi.”

ASUU ta fara yajin aikin ne a ranar 14 ga Fabrairu, 2022, bayan da gwamnatin tarayya ta ki biyan wasu bukatun ta.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp