Kungiyar malaman jami’o’i ta ASUU, ta musanta labarin da ke yawo cewa ta na bukatar Naira 1 daga wajen gwamnatin tarayya.
Shugaban kungiyar na kasa, ya ce, suna yajin aiki ne kan Naira tiriliyan 1.3 da gwamnatin tarayya ta yi musu alkawarin za ta biya duk shekara, amma hakan ya gaza.
TheCable ta rawaito cewa, ASUU ta fada yajin aiki a ranar 14 ga watan Fabrairu bayan kwanaki biyu da suka kwashe suna zantawa a tsakanin shugabannin kungiyar.
Kungiyar ta zargi gwamnati da tozarta yarjejeniyarsu wacce ta sa suka janye yajin aikin da suka yi a shekarar 2020.
ASUU ta kara da cewa ta kara fadawa yajin aiki ne sakamakon halayyar gwamnati kan sasancin da suka nema a fannin albashinsu da alawus dinsu tare da karbar tsarin biyan albashi na University Transparency Accountability Solution (UTAS).