fidelitybank

ASUU ta kalubalanci gwamnati a kan karancin kudi da wahalar man fetur

Date:

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), ta soki gwamnatin tarayya kan ƙarancin Kuɗi da na man fetur da ake fama da shi a faɗin ƙasar.

A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar Emmanuel Osodeke ya fitar ya ce gwamnatin ƙasar a matakan tarayya da jihohi da kuma ƙananan hukumomi na aiwatar da tsare-tsaren da suke wahalar da talakawan ƙasar.

Ya ƙara da cewa matakin da Kotun Ƙolin ƙasar ta ɗauka na dakatar da aiwatar da wa’adin 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsofaffin takardun kuɗi, zai taimaka wajen sauƙaka wa ‘yan ƙasar halin matsin da suke ciki.

Mista Osodeke ya ƙara da cewa tsarin da gwamnan CBN Godwin Emefiele ya ɓullo da shi na ”hana walwalar kuɗi” an taɓa yin sa a Indiya a shekarar 2016 wanda ya haifar da wahalhalu a ƙasar.

“Dan haka, ASUU tana yaba wa Kotun Ƙoli da wannan hukunci ta hanyar la’akari da halin da talaka ke ciki wanda Emefiele ya jefa su ciki”, in ji Osodeke.

A makon da ya gabata ne dai Kotun Kolin ƙasar ta dakatar da Babban Bankin ƙasar aiwatar da wa’adin 10 ga watan Fabrairu na daina amfani da tsoffin kuɗin, bayan da wasu jihohin ƙasar uku suka shigar da ƙara gaban kotun.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...
X whatsapp