fidelitybank

ASUU ta kai karar Gwamnati a kan yi mata kishiya

Date:

Kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU za ta kai karar gwamnatin kasar kan rijistar da ta yi wa sabbin kungiyoyi na malaman wato CONUA da NAMDA ( Congress of Nigerian Universities Academics, da National Association of Medical and Dental Academics).

Lauyan kungiyar ta ASUU, Femi Falana, shi ne ya bayyana haka a wata hira ta tashar talabijin na Channels, a yau Alhamis, inda ya ce za su kalubalanci yi wa kungiyoyin biyu rijistar.

A ranar Talata ne ministan kwadago, Chris Ngige, ya bayar da takardar shedar rijista ga sabbin kungiyoyin biyu da ke zaman kamar kishiyoyi ga ASUU.

A lokacin da yake ba su takardar Ngige, ya ce kungiyoyin biyu za su wanzu kafada da kafada da ASUU.

Ita dai ASUU tana yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairu, inda mambobinta wato malaman jami’o’in gwamnati suka dakatar da aiki a kan kin biyansu kudaden alawus-alawus tare da neman kyautata jin dadinsu da sauran bukatu daga gwamnatin tarayya.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar Æ´an Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar ÆŠinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp