Magatakardar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya roki malaman da ke yajin aiki da su koma.
Oloyede ya yi wannan roko ne a ranar Asabar yayin da yake sa ido a kan jarrabawar gama-gari ta 2022 (UTME).
Fiye da É—alibai 42,000 ne suka halarci jarabawar da aka gudanar a cibiyoyi 45 na jihohi biyar.
Oloyede ya yi kira ga bangarorin da su cimma matsaya don ganin daliban da abin ya shafa sun koma azuzuwa.
Magatakardar ya ce, ko ASUU ta janye yajin aikin ba zai hana ta sake faruwa ba.