fidelitybank

ASUU ta gargadi mambobinta kan kiran jami’ar Benue

Date:

Biyo bayan umarnin da mahukuntan Jami’ar Jihar Benue (BSU) suka bayar a ranar Talata, inda suka umurci dukkan ma’aikatan da su koma aiki, nan take.

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU reshen Jihar Binuwai, ta yi kira ga mambobinta da su kwantar da hankalinsu tare da jiran umarnin shugabannin kungiyar.

Hukumar gudanarwa ta BSU a cikin wata sanarwa da magatakardar, Misis Mfaga Modom, ta fitar ta umurci dukkan ma’aikatan makarantar da su koma aiki nan take.

Amma da yake mayar da martani ga umarnin a wata sanarwa a ranar Laraba, ta hannun Terrumun H. Gajir, sakataren ASUU-BSU, ya shawarci mambobin kungiyar da su kwantar da hankula tare da jiran karin umarni.

Kungiyar ta yi gargadin cewa duk wani memba da aka samu ya sabawa yajin aikin zai fuskanci hukuncin ladabtarwa.

A cewarsa, “ASUU-BSU na ci gaba da yajin aiki kamar yadda kungiyar ta kasa ta bayyana”, inda ya kara da cewa takardar ba ta shafi mambobinta ba.

Ya yi kira da a yi taron gaggawa a ranar Alhamis, 29 ga Satumba, 2022, domin tattauna hanyoyin da mambobin kungiyar za su bi.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp