fidelitybank

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Date:

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin aikin da ta ƙudiri aniyar farawa a yau saboda rashin biyan mambobinta albashin watan Yuni.

Tun da farko ƙungiyar ta yi barazanar daina shiga azuzuwan ɗalibai saboda rashin biyansu albashin watan Yunin da ya gabata.

Ƙungiyar ta bayar da wa’adin cewa idan har ba a biya albashin watan a jiya Litinin ba, to za ta dakatar da shiga azuzuwan ɗalibai.

Jaridar Leadership a ƙasar ta ambato, shugaban ƙungiyar reshen Abuja, Dakta Sylvanus Ugoh na cewa an janye matakin ne saboda tuni gwamnati ta fara biyansu albashi.

“Mambobinmu sun fara samun albashinsu na watan Yuni tun a jiya kafin 12:00 na dare, wanda kuma shi ne wa’adin da muka bayar”, in ji shi.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp