fidelitybank

ASUU na iya shelanta yajin aikin sai baba-ta-gani

Date:

Majalisar zartaswar kungiyar malaman jami’o’i ta kasa za ta yi taro a yau Lahadi, domin duba yajin aikin da ke ci gaba da yi.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, daya daga cikin mambobin kungiyar ya ce: “Eh, mun hadu a yau kan yajin aikin da ake yi da sauran su.

Majiyar ta kuma ce, ba zai yiwu a janye yajin aikin ba, inda ta kara da cewa “Babu wani ci gaba mai kyau da na sani.”

Sai dai kuma shugaban kungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke, shi ma ya tabbatar da taron amma bai bayar da cikakken bayani ba.

Taron dai na zuwa ne kwana daya da kare yajin aikin gargadi na wata daya da kungiyar ASUU ta yi.

Wata majiya da ta zanta da PM News ta ce, kungiyar na iya shelanta yajin aikin sai baba-ta-gani saboda Gwamnatin Tarayya ta gaza magance matsalolin da ASUU ta gabatar.

Kungiyar ASUU ta zargi gwamnatin kasar da gaza aiwatar da yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta rattabawa kungiyar a shekarar 2009.

Kungiyar ta ASUU ta kuma zargi gwamnatin tarayya da yunkurin kin tura UTAS, tsarin biyan kudi da ASUU ta tsara a madadin tsarin biyan kudin IPPIS.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp