Majalisar zartaswar kungiyar malaman jami’o’i ta kasa za ta yi taro a yau Lahadi, domin duba yajin aikin da ke ci gaba da yi.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa, daya daga cikin mambobin kungiyar ya ce: “Eh, mun hadu a yau kan yajin aikin da ake yi da sauran su.
Majiyar ta kuma ce, ba zai yiwu a janye yajin aikin ba, inda ta kara da cewa “Babu wani ci gaba mai kyau da na sani.”
Sai dai kuma shugaban kungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke, shi ma ya tabbatar da taron amma bai bayar da cikakken bayani ba.
Taron dai na zuwa ne kwana daya da kare yajin aikin gargadi na wata daya da kungiyar ASUU ta yi.
Wata majiya da ta zanta da PM News ta ce, kungiyar na iya shelanta yajin aikin sai baba-ta-gani saboda Gwamnatin Tarayya ta gaza magance matsalolin da ASUU ta gabatar.
Kungiyar ASUU ta zargi gwamnatin kasar da gaza aiwatar da yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta rattabawa kungiyar a shekarar 2009.
Kungiyar ta ASUU ta kuma zargi gwamnatin tarayya da yunkurin kin tura UTAS, tsarin biyan kudi da ASUU ta tsara a madadin tsarin biyan kudin IPPIS.