fidelitybank

ASUU ki gaggauta koma wa aiki – Kotu

Date:

Kotun Daukaka kara ta umarci kungiyar malaman jami’o’i ta kasa, ASUU, da ta gaggauta komawa bakin aiki ba tare da bata wani lokaci ba.

Hukuncin ya biyo bayan daukaka karar da kungiyar ta yi ne a kan hukuncin da Kotun Kwadago ta kasar ta yi ne inda ta umarci kungiyar ta ASSU da ta kawo karshen yajin aikin da ta kwashe wata bakwai tana yi.

Yayin yanke hukuncin kotun daukaka karar ta ce janye yajin aikin shi ne sharadin kawai da zai sa ta samu damar daukaka kara da ta yi kan hukuncin kotun kwadagon.

A kan hakan ne kotun ta yarda ta saurari daukaka karar amma da sharadin kungiyar ta janye yajin aikin da take yi ba tare da bata wani lokaci ba, kafin a kai ga warware ainahin shari’ar da ake yi kan batun.

Ita dai ASUU tana yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairu, inda mambobinta wato malaman jami’o’in gwamnati suka dakatar da aiki a kan kin biyansu kudaden alawus-alawus tare da neman kyautata jin dadinsu da sauran bukatu daga gwamnatin tarayya.

Gwamatin tarayya ta yi wa wasu sabbin kungiyoyi biyu na malaman jami’a da suka bullo wadanda ke zaman tamkar kishiya ga ASUU.

Kungiyoyi su ne CONUA da NAMDA ( Congress of Nigerian Universities Academics) da (National Association of Medical and Dental Academics).

Kuma ASUU ta ce za ta kai gwamnati kara kan yi wa kungiyoyin biyu rijista.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp