fidelitybank

ASUU ki gaggauta koma wa aiki – Kotu

Date:

Kotun Daukaka kara ta umarci kungiyar malaman jami’o’i ta kasa, ASUU, da ta gaggauta komawa bakin aiki ba tare da bata wani lokaci ba.

Hukuncin ya biyo bayan daukaka karar da kungiyar ta yi ne a kan hukuncin da Kotun Kwadago ta kasar ta yi ne inda ta umarci kungiyar ta ASSU da ta kawo karshen yajin aikin da ta kwashe wata bakwai tana yi.

Yayin yanke hukuncin kotun daukaka karar ta ce janye yajin aikin shi ne sharadin kawai da zai sa ta samu damar daukaka kara da ta yi kan hukuncin kotun kwadagon.

A kan hakan ne kotun ta yarda ta saurari daukaka karar amma da sharadin kungiyar ta janye yajin aikin da take yi ba tare da bata wani lokaci ba, kafin a kai ga warware ainahin shari’ar da ake yi kan batun.

Ita dai ASUU tana yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairu, inda mambobinta wato malaman jami’o’in gwamnati suka dakatar da aiki a kan kin biyansu kudaden alawus-alawus tare da neman kyautata jin dadinsu da sauran bukatu daga gwamnatin tarayya.

Gwamatin tarayya ta yi wa wasu sabbin kungiyoyi biyu na malaman jami’a da suka bullo wadanda ke zaman tamkar kishiya ga ASUU.

Kungiyoyi su ne CONUA da NAMDA ( Congress of Nigerian Universities Academics) da (National Association of Medical and Dental Academics).

Kuma ASUU ta ce za ta kai gwamnati kara kan yi wa kungiyoyin biyu rijista.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar É—an wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faÉ—an kan iyaka...

Ba mu Æ™ayyade shekarun shiga Æ™aramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman Æ™asar ta amice da Æ™asar FalasÉ—inu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naÉ—a Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano É—aure shahararrun...
X whatsapp