fidelitybank

ASUU da Gwamnati ku sasanta kan ku – Kishiyar ASUU

Date:

Sabuwar kungiyar ma’aikatan koyarwa a jami’o’i ta kasa da gwamnati ta yi wa rijista, ta yi kira ga takwararta kungiyar ASUU ta cimma masalaha da gwamnati don dalibai su koma daukan darasi a azuzuwa.

Sabuwar kungiyar ta ce ita ba ta yajin aiki, duk da haka tana kira ga gwamnatin tarayya da takwararta kungiyar ASUU su sasanta tsakaninsu ta yadda za a bude jami’o’i, don harkokin koyo da koyarwa su ci gaba.

Babban jami’in kungiyar CONUA na kasa, Niyi Sunmonu ne ya yi wannan kira lokacin da yake zantawa a cikin shirin Sunrise Daily na gidan talbijin din Channels a ranar Laraba.

Jami’in ya kuma yi kira da a rika tuntubar dukkan kungiyoyi masu rijista cikin harkokin da ake da wata matsala game da su. A ranar Talata ne, ministan kwadagon Najeriya Chris Ngige ya bai wa kungiyar CONUA da ta NAMDA rijistar zama halattattun kunyoyin malaman jami’o’i a kasar.

Tashar Channels ta ambato ministan yana cewa kungiyoyin biyu za su rika gudanar da harkokinsu ne tare da ASUU, haka kuma sabbin kungiyoyin za su ci gajiyar duk wani hakki da alfarma kamar yadda ake bai wa duk wata kungiyar malaman manyan makarantu.

Tun a tsakiyar watan Fabrairun 2022 ne kungiyar ASUU ta tsunduma yajin aiki don nuna bijirewa kan rashin biyan kudade alawus-alawus da rashin kyautata jin dadin malamai da sauransu.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Za mu ladabtar da Jami’an mu da aka gansu suna taimakawa ‘yan siyasa a Kano – ‘Yansanda

Rundunar Æ´an sanda ta jihar Kano ta ce, ta...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baÉ—ala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...

NNPP ta yi tafka magudi a zabencike gurbin Kano – Farouk Lawan

Tsohon dan majalisar wakilai, Farouk Lawan, ya yi zargin...

Dan shugaban kungiyar Boko Haram ya shiga hannu

Hukumomi a ƙasar Chadi sun kama yaron shugaban ƙungiyar...

Daga yau wankin koda a Najeriya ya koma dubu 12 maimakon dubu 50 – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya amince da rage farashin...

An ceto Mutane 25 da syka kife a kwale-kwalen Sokoto

Hukumomi a jihar Sokoto sun ce, sun samu nasarar...

An fara duba rabon gyaran arzikin Najeriya

Shugaban Hukumar rarraba arziƙin ƙasa RMAFC, Mohammed Shehu, ya...
X whatsapp