Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar, ya ce, kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ba ta da wasu dalilai da za su iya ci gaba da yajin aikin.
Badaru ya bayyana haka ne a lokacin da yake ganawa da manyan sakatarorin dindindin, daraktoci, mataimakan daraktoci, da shugabannin ma’aikatu da na kananan hukumomi a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake Dutse.
Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake mayar da martani kan yajin aikin da kungiyar ASUU Sule Lamido ke yi, reshen Kafin-Hausa a jihar Jigawa.
Ya bayyana cewa ASUU a jami’ar mallakar gwamnati ba ta da dalilin ci gaba da yajin aikin.
“Ban ga dalilin da zai sa jami’o’in jihar su ci gaba da yajin aikin saboda kamar yadda gwamnatin jihar ta riga ta biya musu bukatunsu kamar lokacin da ya kamata.
“Kusan kashi saba’in cikin dari na Malamai ‘yan asalin jihar ne da suke tunanin nuna kauna da damuwa ga ilimin shugabanni masu zuwa,” in ji shi.
Gwamna Badaru ya bukaci kungiyar da ta yaba da jajircewar gwamnati kada a yi amfani da su wajen yakin da bai shafe su ba.
Don haka ya bukaci dattawa da sauran masu ruwa da tsaki a jihar su sa baki a yajin aikin da ake yi.
ASUU ta shiga yajin aikin ne a ranar 14 ga Fabrairu, 2022, kan batun shigar ma’aikatan gwamnatin tarayya a IPPIS, sai dai jami’o’in gwamnatin jihar ba su da alaka da IPPIS tunda albashin su baya zuwa daga gwamnatin tarayya.