fidelitybank

Asusun Najeriya na waje ya ƙaru zuwa dala biliyan 34 da miliyan 100 – CBN

Date:

Babban Bankin Ƙasa CBN ya sanar da cewa, ya kammala biyan daukacin kudaden kasashen waje da suka makale a hannunsa wadanda aka tantance halaccinsu.

Bankin ya sanar da hakan jiya Laraba a cikin wata sanarwa daga mai magana da yawunsa Hakama Sidi Ali.

A cewar mai magana da yawun babban bankin, an tura wa bankunan kasuwanci na kasar Dala biliyan daya da rabi a kwanan nan a zaman kason karshen na biliyoyin dalolin mallakin ‘yan kasuwa da kamfanoni da suka makale a hannunsa saboda karancin dala.

Ta ce aikewa da kudin ya biyo bayan wani aikin tatancewa na kwa-kwaf da wani kamfani mai zaman kansa ya yi, inda aka tabbatar da sai hada-hadar da aka yi da gaske ne aka biya kudin da aka yi ta.

Ta ce kuma nan take an tura duk wata hada-hadar da ake da shakku kanta zuwa ga masu bincike domin sake duba ta.

Da farkon dai dala biliyan bakwai ce masu bin bashin suka yi ikrarin sun makale a hannun babban bankin, to amma daga bisani binciken da wannan kamfanin ya yi ya gano cewa babu gaskiya a ikrarin, dala biliya 2 da miliyan 400 daga cikin biliyan bakwai din saboda babu wasu takardun shaidar yin hada-hadarsu.

Bankin ya ce manufar daukar matakin biyan bashin ita ce daidaita kasuwar canjin kudi ta kasar abin da zai taimaka wajen sauko da farashi da kuma ba masu saka-jari kwarin gwiwa.

Bankin na CBN ya kuma sanar da cewa kudaden da ke a asusun ajiya na kasashen waje na kasar sun karu zuwa dala biliyan 34 da miliyan 110, karuwa mafi yawa a cikin watanni takwas.

CBN ya ta’allaka haka ga karuwar turo kudade zuwa kasar da ‘yan Najeriya ke yi daga kasashen waje, da kuma karuwar sayen hajoji na cikin gida da masu saka jari da saka jari daga waje ke yi.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp