Gwamnatin jihar Kaduna ta shawarci mahukuntan dukkan asibitocin gwamnati da su bi dokar hana biyan kudi da kuma karbar kudin ta na’urar sadarwa.
Tun kafin musanya kudin kasa a halin yanzu, Hukumar Harajin Cikin Gida ta Jihar Kaduna ta soke tare da haramta biyan kudade kamar yadda dokar hana haraji ta jihar Kaduna ta 2020 ta tanada.
Karanta Wannan: Za mu yi maganin ‘yan bani na iyan Buhari – El-Rufa’i
“Saboda haka, babu wani dalili da zai sa asibitocin gwamnati su yi watsi da musayar kudi na lantarki,” in ji Shugaban Hukumar KADIRS, Dakta Ziad Abubakar, a ranar Asabar a Kaduna.
Yana mai da martani ne kan korafe-korafen da ma’aikatan wasu asibitocin gwamnati suka yi na cewa a biya su kudaden ayyukan da aka yi.