fidelitybank

Asibitin Aminu Kano ya yi tir da likitan da ya yi sakaci da lafiyar jariri

Date:

Hukumar Asibitin Koyarwa na Aminu Kano ta yi Allah wadai akan sakacin da wani likita ya yi lokacin da yake kula da lafiyar wani jariri.

A cikin wata takarda mai dauke da sa hannun, Hauwa Muhd Abdullahi, Shugabar Sashen Hurda da Jama’a na Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, ta ce, Jaririn wadanda aka haifa makon da ya gabata ya zo da wata matsala wadda ta bukaci yi masa gwaji ta hanyar daukar jininsa a inda likitan ya shiga dimuwa wanda ya haifar da abin da ya faru.

Hukumar Asibitin ta girgiza da Jin Wannan mugun labari Wanda a shekaru talatin da uku da kafuwar Asibitin Hakan bai tabar faruwa ba. Hukumar tana jajentawa iyayen wannan jariri bisa ga abin da ya faru.

A Kuma halin da ake ciki an mika wa kwamitin da yake bibiyar matsalolin badakala da sakacin aiki wato (Committee on Negligence of Duty)domin yin zurzurfan bincike tare da daukan mataki akan duk Wanda yake da hannu a cikin wannan sakaci da ya faru.

Shugaban Asibitin Koyarwan farfesa Abdurrahman Abba Sheshe, ya yi kira ga duk mara lafiya ko Yan Uwan marasa lafiyan da su ga ba su gamsu da yadda ake kula da lafiyar su ko ta Yan Uwansu ba, da su yi gaggawa wajen sanar da hukumar Asibitin ta Hanyar jami’anta wadanda ake kira da( Servicom Desk Officers).

Ya ce, Asibitin yan a da irin wadannan jami’i kimanin Arbanin, wadanda aka raba su a sassan gudanar da aiki daban daban a cikin Asibitin.Baya ga sashen hurda da Jama’a da wajen Matron-Matron na dakin kwanciya wadanda suke aiki tsawon awa ashirin da biyar.
Farfesa Abdurrahman,ya kara da cewa ta Hanyar mika korafi ne kawai hukumar Asibiti za ta iya kamowa tare da hukumta masu laifi.

Ya Kuma Yi kira ga Mahaifin wannan jariri da ya taimaka wajen isar da makamancin wannan korafi ga kwamitin binciken ko Kuma sashen hurda da Jama’a na Asibitin.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maÆ™ale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp