fidelitybank

Asibitin Aminu Kano ya yi tir da likitan da ya yi sakaci da lafiyar jariri

Date:

Hukumar Asibitin Koyarwa na Aminu Kano ta yi Allah wadai akan sakacin da wani likita ya yi lokacin da yake kula da lafiyar wani jariri.

A cikin wata takarda mai dauke da sa hannun, Hauwa Muhd Abdullahi, Shugabar Sashen Hurda da Jama’a na Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, ta ce, Jaririn wadanda aka haifa makon da ya gabata ya zo da wata matsala wadda ta bukaci yi masa gwaji ta hanyar daukar jininsa a inda likitan ya shiga dimuwa wanda ya haifar da abin da ya faru.

Hukumar Asibitin ta girgiza da Jin Wannan mugun labari Wanda a shekaru talatin da uku da kafuwar Asibitin Hakan bai tabar faruwa ba. Hukumar tana jajentawa iyayen wannan jariri bisa ga abin da ya faru.

A Kuma halin da ake ciki an mika wa kwamitin da yake bibiyar matsalolin badakala da sakacin aiki wato (Committee on Negligence of Duty)domin yin zurzurfan bincike tare da daukan mataki akan duk Wanda yake da hannu a cikin wannan sakaci da ya faru.

Shugaban Asibitin Koyarwan farfesa Abdurrahman Abba Sheshe, ya yi kira ga duk mara lafiya ko Yan Uwan marasa lafiyan da su ga ba su gamsu da yadda ake kula da lafiyar su ko ta Yan Uwansu ba, da su yi gaggawa wajen sanar da hukumar Asibitin ta Hanyar jami’anta wadanda ake kira da( Servicom Desk Officers).

Ya ce, Asibitin yan a da irin wadannan jami’i kimanin Arbanin, wadanda aka raba su a sassan gudanar da aiki daban daban a cikin Asibitin.Baya ga sashen hurda da Jama’a da wajen Matron-Matron na dakin kwanciya wadanda suke aiki tsawon awa ashirin da biyar.
Farfesa Abdurrahman,ya kara da cewa ta Hanyar mika korafi ne kawai hukumar Asibiti za ta iya kamowa tare da hukumta masu laifi.

Ya Kuma Yi kira ga Mahaifin wannan jariri da ya taimaka wajen isar da makamancin wannan korafi ga kwamitin binciken ko Kuma sashen hurda da Jama’a na Asibitin.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

ÆŠanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon É—antakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuÉ—i dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a Æ™auyuka 15 na Zamfara a mako É—aya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huÉ—u ne suke biyan mafi Æ™arancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp