fidelitybank

Asibitin AKTH ya fara yi wa Yara masu fama da cutar ɓurma hanci 200 tiyata kyauta

Date:

Asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH), ya fara yi wa majinyata 200 tiyatar burma hanci kyauta a fadin kasar nan.

Aikin tiyatar wanda gidauniyar Qatar Charity Foundation ta dauki nauyin shi na da nufin rage radadin da kananan yara ke fama da shi da kuma ba su damar rayuwa mai inganci.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da aikin tiyatar, Daraktan kasar a gidauniyar Qatar Charity, Hamdi Abdou ya ce “munyi nasarar gudanar da aikin tiyatar burma hanci ga dimbin yara a Pakistan, Somalia da Ghana. A yanzu mun himmatu wajen fadada wannan shiri a Najeriya, da nufin amfanar da kimanin yara 200 a fadin kasar nan.”

Ya ce ayyukan da gidauniyar keyi a Najeriya ya wuce aikin tiyatar burma hanci ta hada harda aikin ido da ginin asibitoci, tiyatar zuciya da tallafin kayan aikin likitanci na asibiti da sauran su.

“Dukkan wadannan yunƙurin na samuwa ne ta hannun ƙwaƙƙwaran jagoranci na Qatar Charity – Nijeriya da kuma ƙarƙashin jagoranci da goyon bayan Jakadan Qatar a Nijeriya, Dakta Ali bo Cihanem Al Hajri.” A cewarsa.

A nasa jawabin, Babban Daraktan asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Farfesa Abdurahman Abba Sheshe ya bayyana cewa ana sa ran yin tiyatar yara 200 cikin watanni uku kyauta, yace za’a basu magani tare da ciyarwa yayin zaman jinyar da zasuyi kyauta.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp