fidelitybank

Asibitin AKTH ya fara yi wa Yara masu fama da cutar ɓurma hanci 200 tiyata kyauta

Date:

Asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH), ya fara yi wa majinyata 200 tiyatar burma hanci kyauta a fadin kasar nan.

Aikin tiyatar wanda gidauniyar Qatar Charity Foundation ta dauki nauyin shi na da nufin rage radadin da kananan yara ke fama da shi da kuma ba su damar rayuwa mai inganci.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da aikin tiyatar, Daraktan kasar a gidauniyar Qatar Charity, Hamdi Abdou ya ce “munyi nasarar gudanar da aikin tiyatar burma hanci ga dimbin yara a Pakistan, Somalia da Ghana. A yanzu mun himmatu wajen fadada wannan shiri a Najeriya, da nufin amfanar da kimanin yara 200 a fadin kasar nan.”

Ya ce ayyukan da gidauniyar keyi a Najeriya ya wuce aikin tiyatar burma hanci ta hada harda aikin ido da ginin asibitoci, tiyatar zuciya da tallafin kayan aikin likitanci na asibiti da sauran su.

“Dukkan wadannan yunƙurin na samuwa ne ta hannun ƙwaƙƙwaran jagoranci na Qatar Charity – Nijeriya da kuma ƙarƙashin jagoranci da goyon bayan Jakadan Qatar a Nijeriya, Dakta Ali bo Cihanem Al Hajri.” A cewarsa.

A nasa jawabin, Babban Daraktan asibitin koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Farfesa Abdurahman Abba Sheshe ya bayyana cewa ana sa ran yin tiyatar yara 200 cikin watanni uku kyauta, yace za’a basu magani tare da ciyarwa yayin zaman jinyar da zasuyi kyauta.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp