fidelitybank

Ashe Tinubu ba shi da lafiya Atiku kuma ya tsufa – Rev Kelvin

Date:

Wani fitaccen malamin cocin Katolika, Rev Fr Kelvin Ugwu, ya mayar da martani ga faifan bidiyon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Asiwaju Bola Tinubu, da takwaransa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Tinubu ya saka wani ɗan gajeren bidiyo na kansa a kan keken motsa jiki a yammacin Lahadi don karyata jita-jita da ake yadawa cewa ba shi da lafiya sosai.

Hakazalika, hoton Atiku wanda ya dauke shi yana rawa da wakar wani mawakin Najeriya, shi ma ya bazu a ranar Lahadi.

Da yake mayar da martani, Fr Kelvin, wani limamin mishan da ke aiki a wajen kasar, ya fada a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook da aka tabbatar cewa faifan bidiyon ya fallasa raunin ‘yan takarar shugaban kasa biyu.

Ya rubuta, “Ban taba sanin Atiku wannan tsoho ne ba. Ban taba sanin Tinubu ba shi da lafiya. Bidiyon na rawa ya fallasa Atiku a matsayin wanda ya tsufa kuma mai rauni.

“Bidiyon keken ya fallasa Tinubu a matsayin wanda ke fama da rashin lafiya kuma yana buƙatar tantancewa da kowane bidiyo, koda kuwa tsohon bidiyo ne.

“Babban matsalar da ke tattare da su duka ita ce kwadayi. Babbar matsalar su biyun ita ce na kusa da su sun fi kwadayi. Sun yi nasarar kewaye kansu da sycophants da parasites fiye da masoya na gaskiya da gaske waɗanda za su gaya musu gaskiya a fuskokinsu.

“Abin farin ciki shine muna da madadin. Tun da dadewa ba a taba samun karfi na uku a zabukanmu ba, ba mu samu damar sanya mutumin a tsakiya ba”.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp