fidelitybank

Arsenal za ta yi rashin Gabriel bisa doguwar jinya

Date:

Ɗan wasan baya na ƙungiyar Arsenal Gabriel Magalhaes zai yi jinya zuwa karshen kakar wasanni ta bana, bayan samun rauni a cinyarsa.

An sauya ɗan wasan ɗan asalin Brazil a wasan da Arsenal ta doke Fulham da 2-1 a gasar Premier ranar Talata a Emirates.

Toshon ɗan wasan na Lille ya buga wasanni 28 cikin 30 na gasar Premier ta bana, inda Arsenal ɗin ta zama wadda ba a ci kwallo da yawa ba a bana – inda aka ci ta kwallo 25 kaɗai a gasar.

“Za a yi wa Gabi tiyata a cinyarsa a cikin kwanaki masu zuwa, kuma nan da zai fara karɓar horo na musamman don ƙoƙarin dawowa a farkon kakar wasa ta baɗi,” in ji sanarwar da Arsenal ta fitar.

Ƙungiyar tana mataki na biyu a teburin gasar Premier, maki 12 a bayan Liverpool – inda ya rage wasanni takwas a kammala kakar bana.

Gunners ɗin na shirin tunƙarar Real Madrid a matakin wasan daf da na ƙarahe na gasar zakarun Turai.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp