Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta kwace ragamar Kyaftin din kungiyar daga hannun dan wasan ta, Pierre-Emerick Aubameyang, sakamakon keta da’a, da ya yi.
An ajiye dan wasan mai shekaru 32 a wasan da suka doke Southampton da ci 3-0 a ranar Asabar, kuma ba zai buga wasan da West Ham za ta ziyarci Emirates ranar Laraba ba.
“Bayan saba masa na ladabtarwa a makon da ya gabata, Pierre-Emerick Aubameyang, ba zai ci gaba da zama kyaftin din kungiyar ba, kuma ba za a yi la’akari da shi ba a wasan da za su yi da West Ham United ranar Laraba”. inji Arsenal a cikin wata sanarwa.
“Mu na sa ran dukkan ‘yan wasanmu, musamman kyaftin din mu, su yi aiki da bin ka’idojin da muka tsara kuma muka yarda.”
A cewar The Athletic, Aubameyang ya dawo daga baya fiye da yadda aka amince da shi daga balaguron sirri da ya yi zuwa Faransa a makon da ya gabata, wanda daga baya ya tilasta masa barin daukar horo, saboda bukatar wuce ka’idojin coronavirus.
Haka kuma kociyan kungiyar Mikel Arteta bai bar Aubameyang ba, saboda nasarar da suka samu a Arewacin Landan da Tottenham a watan Maris kan batun ladabtarwa a lokacin da ya isa a makare, domin wani taron share fage.